1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Za a yi zama na musamman kan Siriya

Ahmed Salisu
May 8, 2019

Kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya zai yi wani zama na musamman a ranar Juma'ar da ke tafe domin tattaunawa kan karuwa fadan da ake cigaba da samu a yankin Idlib da ke arewa maso yammacin kasar Siriya.

https://p.dw.com/p/3IBj6
Idlib, Attentat des Assad-Regimes auf Wohngebiete in Syriens 
Nach dem Attentat des Assad-Regimes auf Wohngebiete in Syrien
Hoto: picture-alliance/M.Ali

Kasashen Beljiyam da Jamus da kuma Kuwait ne suka bukaci da a yi wannan zama bayan da Rasha da kuma gwamnatin Siriya din suka matsa kaimi wajen yin luguden wuta a wuraren da masu da'awar jihadi ke rike da su, batun da ya janyo lalacewar asibitoci da makarantu a yankin.

Kimanin mutane miliyan 3 ne ke zaune a birnin na Idlib wanda shi ne birni na karshe da a halin yanzu ba ya karkashin ikon gwamnatin Shugaba Bashar al-Assad.