1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zaman lafiya a Mali na tangal-tangal

Usman Shehu UsmanMay 12, 2015

Ma'aikatar tsaron kasar ta ce an hallaka sojojinta tara aka jikkata wasu 14, yayin wani harin kwantar bawna da 'yan tawaye masu neman ballewa suka kai.

https://p.dw.com/p/1FOS8
Mali Polizeiabsperrung bei Bamako
Hoto: AFP/Getty Images/I. Sanogo

An dai kai harin kwantar bawnanne kan wata kombar motocin soji da ke kan yanya, kusa da birnin Timbuktu, yankin da sojojin Faransa da na MDD suke da sansani. Harin ya zo ne 'yan kwanaki gabanin yarjejeniyar zaman lafiya da MDD ke yunkurin samarwa ta tabbata, a ranar Jumma'a mai zuwa. Tun a watan da ta gabata ne dai, ake samun arangama tsakanin sojojin gwamnatin Mali da 'yan tawayen Abzinawa.