1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jagoran Falasdinawa ya yi wa wasu kasashe bazana

Zulaiha Abubakar MNA
February 2, 2020

Al'ummar kasar Lebanon da Falasdinawa na zanga-zanga a kusa da ofishin jakadancin Amirka da ke kasar Lebanon, inda suke bayyana kyamar shirin gwamnatin Amirka na kawo karshen rikicin Isra'ila da Falasdinawa.

https://p.dw.com/p/3XA0y
Ägypten Kairo Treffen Arabische Liga | Mahmud Abbas, Präsident der Palästinenser & Abo Al Gheit
Hoto: picture-alliance/Zuma Press/APA Images/T. Ganaim

Tun da farko masu zanga-zangar dauke da tutocin Falasdinu sun yi jerin gwano a Arewa maso Gabashin birnin Beirut suna sukar lamirin Amirka duk da irin matakin tsaron da mahukunta suka dauka don tsaron ofishin jakadancin na Amirka.

A ranar Asabar dai ne jagoran Falasdinawa Mahmoud Abbas ya yi barazanar yanke hulda da kasashen Isra'ila da Amirka yayin da yake jawabi a taron shugabannin kasashen Larabawa, bayan ministocin kasashen wajen kasashen na Larabawa sun zargi Amirka da yunkurin mayar da hannun agogo baya a samar da zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya.