1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zanga-zangar adawa da Mugabe

Abdullahi Tanko BalaAugust 26, 2016

'Yan sanda sun tarwatsa gangamin masu adawa da mulkin Robert Mugabe na kasar Zimbabuwe.

https://p.dw.com/p/1JqNi
Simbabwe Proteste der Opposition in Harare
Hoto: picture-alliance/AP Photo/T. Mukwazhi

'Yan sandan Zimbabuwe sun harba hayaki mai sa hawaye a kan shugabannin 'yan adawar kasar Morgan Tsvangirai da tsohon mataimakin shugaban kasar Joice Mujuru yayin da gangamin zanga-zangar adawa da shugaban kasar Robert Mugabe ta rikide zuwa tarzoma.

Tuni Morgan Tsvangirai da Mujuru suka fice daga wurin taron gangamin a motocin su a cewar wadanda suka shaidar da lamarin. A 'yan watannin baya bayan nan dai jami'an tsaron sun zafafa dirar mikiya sakamakon karuwar zanga-zangar adawa da shugaba Mugabe da Jam'iyyarsa ta ZANU-PF yayin da jama'a suke nuna bacin rai kan tabarbarewar tattalin arziki da rashin ayyukan yi da kasar ke fama da su.