1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zanga-zangar nuna adawa da taron G20 a Hamburg

Abdourahamane Hassane
July 2, 2017

Dubban jama'a a birnin Hamburg da ke a arewacin Jamus sun gudanar da wani gangami don nuna adawa da taron kasashe guda 20 masu karfin tattalin arzikin masana'antu watau G20 da za a yi a wannan makon.

https://p.dw.com/p/2fnIe
Protestwelle gegen den G20 Gipfel
Hoto: picture-alliance/dpa/M. Scholz

'Yan sanda sun ce kamar mutane dubu goma ne suka yi zanga-zangar cikin ruwan sanhi a gaban ofishin magajin gari na birnin na Hamburg inda za a yi taron. Daya daga cikin masu gangamin ya soki lamirin kasashen na G20 da cewar su, suka fi kowa fitar da hayakin da ke gurbata muhali a duniya  amma kuma ba sa yin wani yunkuri don rage hayakin.