1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Facebook ya musanta yada labaran karya kan corona

Ramatu Garba Baba
July 17, 2021

Shafin Facebook ya mayar da martani kan zargin da Shugaba Joe Biden na Amirka yayi na cewa shafin ya taka rawa a yada baiyanan karya kan alluran riga-kafin cutar corona.

https://p.dw.com/p/3wbTm
Weltspiegel | Washington, USA | President Biden bekräftigt US Truppenabzug aus Afghanistan
Hoto: Tom Brenner/imago images

Shafin Facebook ya musanta zargin yada labaran karya kan cutar corona ne a matsayin martani kan kalamn da Shugaban Amirka Joe Biden yayi, inda ya zargi shafukan sada zumunta irinsu Facebook din, da yada baiyanan karya kan alluran riga-kafin corona a shafukan na su. 

Furucin Biden ya biyo bayan samun karuwar alkaluma na masu kamuwa da cutar a makon da ya gabata a cikin kasar, inda ya ce annobar na sanadiyyar mutuwar jama'a da dama a sakamakon dogaro da jama'a ke yi, da baiyanan karya kan alluran rigakafin cutar da shafukan sada zumunta kamar Facebook din ke yadawa.

Amirka ta kasance daya daga cikin kasashen duniya da cutar corona ta yi wa illa sosai, kuma kawo yanzu kasar na fadi tashin ganin ta dakile cutar baki daya daga cikin kasar.