1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zargin juyin mulki a jamhuriyyar Bini

March 4, 2013

Bayan zargin hallaka shugaba Yayi Boni da guba, hukumomi sun sake zargin na hannun damansa da yunkurin juyin mulki.

https://p.dw.com/p/17qMG
Benin President Thomas Boni Yayi gives a press conference on October 26, 2012 after the signing of a convention between the European Union and Benin at the presidential palace in Cotonou. EU commission president Jose Manuel Barroso, who spoke alongside Yayi, said on October 26 that the European Union was working to establish a credible army in Mali, where radical Islamists took control of the north after a military coup. European leaders have vowed to back a proposed African force that may be sent to flush out the Islamists, but have said their support will not include EU combat troops. AFP PHOTO / KAMBOU SIA (Photo credit should read KAMBOU SIA/AFP/Getty Images)
Hoto: K.Sia/AFP/Getty Images

Hukumomi a jamhuriyyar Bini sun fadi - a wannan Litinin cewar hamshakin dan kasuwar audugar nan, wanda ake nema ruwa a jallo, da yunkurin yin anfani da guba domin kissan shugaba Thomas yayi Boni na kasar, ana kuma dangantashi da yunkurin juyin mulkin daya yi sanadiyyar tsare wasu mutane biyu a kasar. Patrice Talon, da ke zama tsohon na hannun daman shugaba Yayi, ana zarginsa da kasancewa cikin wadanda ke da hannu wajen yunkurin kifar da gwamnatin shugaba Yayi a wannan Lahadin.

A dai watan Oktoba ne hukumomin kasar ta Bini suka zarge shi da laifin yumkurin da bai yi nasara ba na musayar wani maganin cutar zuciyar da shugaban ke yin anfani da shi da guba domin hallaka shugaban.

Sai dai kuma 'yan adawa a kasar na dasa ayar tambaya dangane da ko hukumomin na yin anfani da wadannan zarge zargen ne domin shafawa masu hamayya da shi kashin kaza. Tuni kuma babban mai gabatar da kara a kasar Justin Gbenameto ya ce suna kan hanyar bayar da sammaci na kasa da kasa domin cafke Talon din.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Mouhamadou Awal Balarabe