1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana ci gaba da alhinin mutuwar Mugabe

Lateefa Mustapha Ja'afar
September 11, 2019

Gawar tsohon shugaban kasar zimbabuwe marigayi Robert Mugabe ta isa Harare babban birnin kasar cikin rakiyara dakarun soja.

https://p.dw.com/p/3PR0W
Bildergalerie Robert Mugabe Simbabwe Afrika
Tsohon shugaban kasar Zimbabuwe marigayi Robert Mugabe Hoto: picture-alliance/dpa

Matar mamacin Grace Mugabe cikin babaken kaya da shugaban kasar Emmerson Mnangagwa na daga cikin dimbin mutanen da suka halarci filin sauka da tashin jiragen sama na kasar, domin tarbar gawarsa. Da yake jawabi ga mutanen da yawansu ya kai 1,000 da suka je tarbar gawar Mugaben, Shugaba Mnangagwa ya bayyana Mugaben a matsayin jagoran juyin-juya halin kasarsu. Rahotanni sun nunar da cewa za a nuna gawar tsohon shugaban da ya kwashe shekaru 37 yana mulki a Zimbabuwen a wuraren tarihi, kafin a binne shi a ranar Lahadi mai zuwa a wani gurin da har yanzu ba a bayyana ba, abin da ke nuna akwai wata a kasa tsakanin iyalan stohon shugaban da gwamnati. Mugabe dai ya rasu ne a ranar Jumma'ar makon da ya gabata, a wani asibiti da ke kasar Singapor yana da shekaru 95 a duniya.