1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ziyara Franck Walter Steinmeir a gabas ta tsakiya

September 7, 2006
https://p.dw.com/p/BukM

Ministan harakokin wajen Jamus, Franck Walter Steinmeir, na ci gaba da ziyara a yankin gabas ta tsakiya.

A yamacin yau ya tantana, da hukumomin Beyruth, a game da guddumuwar Jamus, a yunƙurin sake gina Libanan da yaƙi ya ma, kaca kaca.

Ministan, na tare da tawagar ƙurraru ta fannin ayyukan custum, wanda su ka masanyar ra´ayoyi da takwarorin su na Libanon a game da hanyoyin tafiyar da aiki, a filayen saukar jiragen sama.

Jamus ta bayana aniyar kula da ɓangaren sojojin ruwa na rundunar shiga tsakakni, da Majalisar Dinkin Dunia ta yanke hukunci aikawa a libanon.

Hukumomin Berlin, sun yi hakan domin amsa gayyatar da Libanon ta yi masu, ta hanyar MDD.

A yau ne, Isra´ila ta bayana cire takunkumin da, ta saka, na hana zirga zirga a Libanon, bayan ta samu tabas, daga Majalisar Dinkin Dunia, na hana jigilar makammai, zuwa Hizbullahi daga ƙasashen ketare.

Bayan Kasar Libanon, Steinmeir ya ziyarci Isra´ila domin ci gaban wannan tantannawa.