1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaban Chadi na yakar Boko Haram

Lawan Boukar LMJ
April 6, 2020

Al'ummar Diffa na murna dangane da tasirin da yunkurin kasar Chadi na kakkabe mayakan Boko Haram a yankin Tafkin Chadin da ta kwashe kusan tsawon mako guda ta na yi, ya yi suna masufatan dawowar zaman lafiya.

https://p.dw.com/p/3aXSh
Tschad Idriss Deby
Shugaban kasar Chadi Idriss Deby ItnoHoto: Getty Images/AFP/L. Marin

 A wani taron maneman labarai da ya yi, Shugaba Idriss Deby Itno na Chadi ya ce ya kawo karshen 'yan ta'adda a kasarsa, inda ya ce a yanzu babu ko guda kuma shi kadai ya yi wannan yakin ba tare da kasashe mokwaftansa ba, inda ya ce: "Babu Boko Haram ko guda yanzu a kasar Chadi, mun kwace dukkanin yankunanmu. Sai dai tun da muka fara wanan yunkurin, kasar Chadi ita kadai ta yi wanan yakin."

Yabon gwani ya zama dole

Hassane Bello, daya daga cikin 'yan kungiyar farar hula na yankin Diffa ya bayyanawa DW cewa sun yaba da wannan yunkuri, koda yake ya ce ba su ji dadin rashin saka hannun kasashe makwabtan Chadin ba. Mazauna Diffan dai sun san za a yi hakan, ganin yadda aka yi wa kasar Chadi barna. A hannu guda kuma gwamnatin Jamhuriyar Nijar ita ma ta shirya da nufin kakkabe sauran tsirarun mayakan Boko Haram din da suka shiga kasar da kuma kare dukanin iyakokinta.