1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabon salon koyar da almajirai a Nijar

June 9, 2020

A baya-bayan nan wasu malaman tsangaya na aikata cin zarafi ta hanyar duka irin na kawo wuka gami da muzgunawa ga almajirai a Nijar. Hakan ya sanya kungiyar makarantun tsangaya a kasar daukar mataki.

https://p.dw.com/p/3dVnJ
Die Bettel-Schüler aus Nordnigeria
A Najeriya ma an dauki matakin inganta karatuin tsangaya a baya.Hoto: DW

Wanan mataki dai na zuwa ne a daidai lokacin da sannu a hankai hukumomi da kungiyoyin kare hakkin dan Adam ke bankado ta'asa da aika-aikar da ke faruwa ga wasu almajirai a makarantun tsangaya, musamman wadanda ake turawa ci-rani a tsakanin Jamhuriyar ta Nijar da kuma makwabciyarta Najeriya.

Nigeria Katsina | Coronakrise | Almajiri Vertreibung
Almajirai na fuskantar matsaloliHoto: DW/Y. I. Jargaba

Lamari na baya-bayan nan shi ne na jihar Diffa, inda a yanzu ya mamaye shafukan sada zumunta na zamani. Shugaban kungiyar makarantun allo ta kasa UECN, Malam Mahamadu Ibrahim ya ce tuni kungiyar tasu ta dauki mataki kan wannan matsala. 

Ana iya cewa dai, ya zuwa yanzu dai fargabar da mutane ke ji suke kuma gani daga nesa ta fara kwankwasa masu kofa, ganin yadda a jihar Diffa aka cafke wani malami da ke cin zarafin almajirai.