1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sintirin bai daya na dakarun yankin tafkin Chadi

Abdourahamane Hassane
April 2, 2020

Dakarun Kasashen Nijar da Najeriya da Chadi sun girka kawance hadin gwiwa da nufin kawar da Boko Haram da ke dada kai hare-hare a kasashen.

https://p.dw.com/p/3aMkQ
Nigeria Soldaten Offensive gegen Boko Haram
Hoto: Reuters/J. Penney

Dakarun Kasashen Najeriya da Nijar da kuma Chadi sun kaddamar da wani gagarumin sumame na hadin gwiwa da nufin kawar da kungiyoyin Boko Baram da ISWAP wadanda suka dada kai hare-hare a kan sojojin kasashen a 'yan kwanaki nan. A cikin wata sanarwa da rundunar sojojin Njeriya ta bayyana ta ce bukatar hadin gwiwar na sojojin kasashen na yankin tafkin Chadi ya zama wajibi domin cimma nasarar yaki da Boko Haram. A cikin watan Maris da ya gabata mayakan na Boko Haram sun kashe sojoji sama da 100  a Chadi da kuma Najeriya.