1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kashe fararen hula 51 a arewacin Mali

Zainab Mohammed Abubakar
August 9, 2021

Wasu da ake zargi mayakan jihadi ne, sun kashe fararen hula 51 a yankin arewacin Mali da sojoji 12 a harin kwanton bauna a Burkina Faso da ke makwabtaka.

https://p.dw.com/p/3ylhS
Unruhe in Mali
Hoto: Getty Images/Stringer

Wannan ya tayar da hankalin mahukunta kan tsanantar tashe-tashen hankula a wannan yanki na sahel.

Maharan dai sun afkawa kauyuka uku da ke kan iyakar Mali da Nijar a ranar Lahadi, inda suka kashe dukkan mazauna kauyukan na Karou da Ouatagouna da Daoutegeft.

Maharan kazalika sun lalata gidaje bayan dibar ganima na kaya da shanu da wasu dabbobi. Rahotanni na nuni da cewar, maharan sun zo ne cikin ayari a kan babura dauke da bindigogi.