1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Martanin kasashe da kungiyoyin addinai kan harin Paris

Zainab Mohammed AbubakarJanuary 8, 2015

Duniya na ci-gaba da alhinin harin da wasu mutane uku suka kai kan wata mujallar Faransa da ya kashe mutane 12 tare da raunata wasu masu yawa a ranar Laraba.

https://p.dw.com/p/1EGi9
Ukraine Botschaft Frankreich Kiew Anteilnahme Charlie Hebdo
Hoto: Getty Images/Vasily Maximov

Mujallar dai ta taba wallafa zanen batanci wa Annabi Muhammad. Yanzu haka dai shugabannin kasashen duniya da dama sun yi Allah wadai da wannan harin.

A yanzu haka dai yan sandan kasar na ci gaba da binciken mutanen da suka kai hari, da shekarunsu yake 18 da 32 da 34.

Tun a ranar Larabarce dai aka fara gangami a biranen Turai da dama, domin nuna alhini kan harin na kasar Faransa. Dubban jama'a sun taru a biranen London, Berlin, Brussels, da makamantansu domin tunawa da wadanda suka mutu a harin na Charlie Hebdo.