1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boko Haram ta tsananta hare-hare a arewacin Najeriya

December 6, 2018

Hankulan al'ummomi a jihohin Borno da Yobe sun tashi ganin yadda Boko Haram ke kai hare-hare ba kakkautawa a sansanonin sojoji da kuma garuruwa duk da komawar manyan hafsoshin sojojin Najeriya yankin Arewa maso Gabas.

https://p.dw.com/p/39ZrI
Mutmaßlicher Boko-Haram-Angriff in Nigeria
Hoto: picture-alliance/AP/Jossy Ola

An yi fatan cewa zuwan da Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi jihar Borno za a samu sauki hare-hare daga Boko haram amma kullum abin karuwa ya ke yi.
Har wayau gwamnatin Najeriya ta bukaci manyan hafsoshin sojojin kasa da da na sama da su koma da zama a shiyyar Arewa maso Gabashn kasar har sai al’amuran tsaro sun inganta lamarin da masana da masharhanta ke ganin ba zai haifar da komai ba tun da ba karo na farko kenan da gwamnatin ke ba da irin wanna umurni ba.