1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gobara ta kashe dalibai a Jamhuriyar Nijar

Abdul-raheem Hassan SB
November 8, 2021

Kimanin kananan yara 24 sun mutu sakamkon tashin gobara a wata makaranta a Maradi da ke Jamhuriyar Nijar inda hukumomin gwamnati suka ce kusan dalibai 80 maza da mata sun samu raunika sakamakon konewa.

https://p.dw.com/p/42k2z
Nigeria Jangebe 300 Schulmädchen von bewaffneten Männern entführt
Hoto: Sunday Alamba/AP/picture alliance

Gobarar ta tashi ne a azuzuwa uku da aka yi su da katakai a kudancin jihar Maradi, zuwa yanzu dai ba a tabbatar da musabbabin tashin gobarar ba.

Bangaren ilimi dai a Jamhuriyar Nijar ba ya samun kaso mai tsoka, matakin da ke da nasaba da rashin wadatattun makarantun boko masu inganci a kasar. Sai dai shugaban kasar na yanzu Mohamed Bazoum ya sha alwashin farfado da harkar ilimi a kasar.