1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dubban magoya bayan 'yan adawa sun amsa kira a Yamai

Salissou Boukari
November 11, 2018

A wannan Lahadin ne dubban jama'a suka fito a birnin Yamai domin amsa kiran 'yan dawa wajen nuna adawarsu da kundin zaben kasar ta Nijar da suke zargin bangaran gwamnati da shirya manakisa a game da zaben.

https://p.dw.com/p/384EE
Niger Demonstration für Bildungsreform
Hoto: picture-alliance/AA/B. Boureima

Tsohon shugaban kasar ta Jamhuriyar Nijar Alhaji Mahamane Ousmane ne dai ya jagorancin wannan zanga-zanga wadda wasu ke fadin ba'a taba ganin irinta ba daga cikin jerin zanga-zangar da 'yan adawan ke shiryawa a birnin na Yamai. Wani kudiri ne dai mai lamba takwas na kundin zaben kasar ta Jamhuriyar Nijar ke kan gaba wajen haddasa cecekuce a kasar. Wannan kudiri kuma ka iya haramta wa madugun 'yan adawan kasar Hama Amadou tsayawa takara a zabukan kasar masu zuwa abin da 'yan adawar na Nijar suka ce ba za ta sabu ba.