1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar za ta iya dakile takunkumin ECOWAS

Abdullahi Tanko Bala
August 14, 2023

Sabon Firaministan Nijar da sojoji suka nada Ali Mahaman Lamine Zeine a wata hira da DW ya ce kasarsa za ta iya dakile takunkumin da ECOWAS ta kakaba mata sakamakon juyin mulkin da sojoji suka yi a kasar

https://p.dw.com/p/4V8xX
Niger Ali Mahaman Lamine Zeine Interview
Hoto: DW

Firaminista Ali Mahaman Lamine Zeine ya shaida wa tashar Deutsche cewa ko dayake kalubale ne wanda babu adalci a cikinsa kakaba musu takunkumi, amma za su iya shawo kansa.

Kungiyar raya ci gaban tattalin arzikin kasashen Afrika ta yamma ECOWAS ta sanya wa Nijar takunkumi bayan juyin mulki kuma ba ta fidda yiwuwar amfani da karfi a kan sojojin da suka kifar da gwamnatin zababben shugaba na dimukuradiyya Bazoum Mohammed ba

Kasashen kungiyar sun katse harkokin kudade da wutar lantarki da kuma rufe iyakokinsu da NIjar.

Tun da farko sojojin sun ce takunkumin ya kuntata wa jama'a ta hanyar rashin samun magani da abinci da wutar lantarki inda suka baiyana matakin da cewa haramtacce ne na rashin imani da kuma rashin tausayin al'umma.

Sai dai Zein ya baiyana kwarin gwiwa da ziyarar tawagar Najeriya inda ya kara jaddada muhimmancin dangantaka tsakanin Nijar da Najeriya da sauran kasashen yammacin Afirka.

Ya kuma bukaci jama'a su nuna amincewa da sabbin mahukuntan kasar ta Nijar