1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Salon rayuwaNajeriya

Najeriya da Nijar: Shirin bikin Kirsimeti

Ibrahima Yakubu Salisu Kaka/LMJ
December 22, 2023

A daidai lokacin da tsadar rayuwa sakamakon faduwar darajar Naira ke shafar shirye-shiryen bikin Kirsimeti a Najeriya, a makwabciyarta Nijar juyin mulkin sojoji ne ya haddasa tsadar rayuwar da ke shafar bikin na bana.

https://p.dw.com/p/4aVJR
Najeriya | Nijar | Kirsimeti | Tsadar Rayuwa | Takunkumi
Tsadar rayuwa ta shafi shirye-shiryen Kirsimeti a Najeriya, a Nijar kuuwa takunkumiHoto: DW/G. Hilse

Yayin da 'yan mata ke zuwa wuraren yin kwalliya da gyaran fatar jiki cikin yanayin da kowa ke kokawa da tsadar kayayyaki sakamakon faduwar darajar Naira da hauhawar farashin kudin kasashen ketare da ke shafar harkokin kasuwancin Najeriya, a bangare guda samari na tserewa 'yan matan ne a irin wannan lokacin saboda tsadar rayuwar. Sai dai yayin da a Najeriyar ake kokawa da tsadar rayuwa sakamakon hauhawar farashin da kuma masassarar tattalin arziki, a makwabciyarta Jamhuriyar Nijar juyin mulkin da sojoji suka yi ne ya jefa al'umma cikin tasku.

Ivory Coast | Abidjan | Kirsimeti
Kaksashen Afirka da dama, kan kawata wurare gabanin KirsimetiHoto: Reuters/L. Gnago

Jim kadan bayan juyin mulkin ne dai, kungiyar Habaka Tattalin Arzikin Kasashen Afirka ta Yamma wato ECOWAS ko CEDEAO ta kakaba takunkumin mai zafi kan Nijar din. Sai dai wannan takunkumi ba wai sojojin da sukaa kifar da gwamnatin ya fi shafa kai tsaye ba, al'ummar kasar ne ke dandana kudarsu. Matsin tattalin arzikin da takunkuman suka haifar dai, ya sanya a bana mabiya Addinin Kirista a Jamhuriyar ta Nijar za su yi bukuwan Kirsimetin cikin halin tasku. Daga cikin matsalar takunkumin dai har da batun rufe kan iyakokin kasar, sai dai duk da wannan halin matsinmabiya Addinin Kirista a Nijar din sun kuduri aniyar yin adu'o'in samun sauki kan halin da kasar ke ciki.