1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tattaunawa da tsagerun Niger Delta ta ci tura a Najeriya

Muhammad Bello/YBJuly 4, 2016

Tattaunawar da ke gudana tsakanin bangaren gwamnatin Najeriya da 'yan bundigar yankin Niger Delta ta fada rudani, inda yanzu 'yan bundigar suka koma bude wuta.

https://p.dw.com/p/1JIvB
Niger Kämpfer
'Yan fafutikar na Niger Delta dai sun matsa kai hare-hare a kadarorin gwamnati da na kasashen wajeHoto: picture-alliance/dpa

Gwamnati dai ta ce har yanzu ta gaza sanin kungiyoyin 'yan bundigar da za a tattauna da su, bisa la'akari da yadda wadannan kungiyoyi ke ta bullowa dabam-dabam.

A wannan Litinin kungiyar Niger Delta Avengers ta ce ta kai jerin hare-hare har biyar a kan kamfanonin man Chevron da NNPC a yankin, kuma ta ce za ta cigaba da kai hari. Hare-haren dai sun zo ne a daidai lokacin da ake tunanin cewar akwai yarjejeniyar tsagaita wuta.

Kungiyar dai ta Avengers da tafi kaurin suna a yanzu, ta nunar da cewa ba ta taba wani zaman tattaunawa da wakilan gwamnati ba, inda kuma gwamnatin kasar ke nuna cewa kawo yanzu ta gaza tantance bangaren 'yan bundigar da za a ainihin tattauna da su, a sakamakon yadda kungiyoyin 'yan bundigar ke dada bullowa a yankin.

Karikatur Gespräche mit Militanten im Niger-Delta?
Shugaba Buhari dai na fama da tarin matsaloli kan rikicin da Najeriya ta shigaHoto: DW

Wani da ke da jibi da wadannan 'yan fafutika masu kai hare-hare da kuma bai yarda da bayyana sunansa ba, ya bayyana wa wakilin DW a yankin cewar lallai kam gwamnatin tarayya ta yi ta ganawa da bangarori da dama a yankin, sai dai kuma fa ba wai da kungiyar ta Avengers ba.

A wani yanayi me nuna cewar al'amarin tsaro a sassan ayyukan na mai cikin surkukin ruwayen na Niger Delta ya sake damewa, shi ne na sanarwar kamfanin aikin mai na Agip da safiyar Litinin, cewar wasu 'yan bundiga a cikin surkukin yankin na shiyyar garin Nembe sun bundige wasu Jami'ansu uku har lahira, kuma wasu a cikin Jami'an sun jikkata matika.

Yanzu dai in har wadannan hare-hare suka ci gaba, to labudda akwai nakasu ga sanarwar da gwamnati ta yi a satin da ya gabata, na cin alwashin tunkarar ayyukan hako danyan mai gadan-gadan.