1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tsamin dangantakar siyasa a Nijar

Abdoulaye Mamane AmadouJanuary 6, 2015

'Yan adawar Nijar din dai na zargin bangaren gwamnati da cin hanci da karbar rashawa tare da yunkurin wargaza jam'iyyun adawar kasar.

https://p.dw.com/p/1EFct
Niger Mahamadou Issoufou und Hama Amadou
Hoto: BOUREIMA HAMA/AFP/Getty Images

A baya-bayan nan dai 'yan adawar kasar sun dauki matakan kauracewa duk wani goron gayyatar da bangaren masu mulki ya yi musu, saboda dalilai na siyasa.

To sai dai a nata bangare, jam'iyyar PNDS tarayya dake mulki na mai ganin rashin abun fadi ne kawai ke ga 'yan adawar. Wannan lamari na faruwa ne a yayin da ake shirin tunkarar zabubbuka a kasar a shekara ta 2016 mai gabatowa.

Tsamin dangantakar dai ya faro ne tun lokacin da masu adawa a Nijar din suka zargi bangaren mulkin da rashin iya jagoranci da cin hanci da rashawa da yin almundahana da dukiyar kasa har da kokarin wargaza jam'iyyun adawa a kasar da nufin ci gaba da kasancewa a kan mulki.

Abdoulaye Mamane Amadou