1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sahel: Taron kan tsaro

February 12, 2021

Chadi za ta jibge dakaru dubu a iyakokin jamhuriyar Nijar da barkina Faso da kuma Mali domin kawo karshen ayyukan masu ikirarin jihadi.

https://p.dw.com/p/3pHH1
Mauretanien G5 Sahel Taskforce
Hoto: Getty Images/AFP/T. Samson

A kokarinta na kawo karshen hare-haren da masu ikirarin jihadi ke kaiwa a yankin Sahel, gwamnatin Chadi za ta kara yawan dakarunta a iyakokin kasashen Jamhuriyar Nijar da Burkina Faso da Mali.

Kimanin dakarun sojin dubu ne  ake sa ran rarrabawa a iyakokin, bayan da Chadin ta yi tunanin agazawa dakarun Faransa da na Tarayar turai da ke aikin wanzar da zaman lafiya a yankin.

Kasar ta Chadi ta ce za ta yi bayanin dalla-dalla yadda rabon zai kasance a wajen taro kan matsalar tsaron yankin da za a gudanar a mako mai zuwa a Birnin N'jamena.

A shekarar da ta gabata dai Faransar ta yi ikirarin samun nasara kan mayakan jihadin da ke tada zaune tsaye a yankin.