1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zaman zullumi saboda rashin kammala zabe a wasu jihohi

Mohammad Nasiru Awal
March 14, 2019

Rashin kammala zaben gwamnoni a wasu jihohin Najeriya guda shida bayan zaben ranar 9 ga watan Maris ya janyo rashin tabbas da zaman dar-dar.

https://p.dw.com/p/3F2CZ
Nigeria Regionalwahlen 2019 | Proteste in Rivers
Hoto: Getty Images/AFP/U. Ekpei

Ana cikin zaman zullumi sakamakon rashin kammaluwar zaben gwamnoni a wasu jihohi shida na Najeriya da suka hada da Kano, Sakkwato, Benue, Bauchi, Adamawa da Filato. Yanzu haka dai hukumar zaben kasar mai zaman kanta wato INEC ta sanya ranar 23 ga watan Maris zama ranar da za a gudanar da zabe a wadannan jihohi.