1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yunkurin magance rikicin Sudan ta Kudu

January 2, 2014

Kasashen yankin gabashin Afirka na kokarin ganin sun kawo karshen rikicin Sudan ta Kudu da ya kwashe tsahon makwannin uku, wanda kuma ya haddasa asarar rayuka da dama.

https://p.dw.com/p/1AkXC
Hoto: Samir Bol/AFP/Getty Images

Bangarorin dake gaba da juna a Sudan ta Kudu na shirin fara tattaunawar sulhu a Addis Ababa babban birnin kasar Habasha, a wani sabon mataki na kawo karshen yakin da suke gwabzawa a tsakaninsu.