1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ba a rabu da Bukar ba a kasar Burundi

Mouhamadou Awal BalarabeMay 14, 2015

'Yan Burundi da ke goyon bayan yunkurin juyin mulki da kuma 'yan gani kasheni na Pierra Nkurunziza suna ci-gaba da kai ruwa rana kan tazarcen shugaban kasa.

https://p.dw.com/p/1EqtF
Militärputsch in Burundi
Hoto: Reuters/G. Tomasevic

Tsohon shugaban hukumar leken asirin Burundi Janar Godefroid Niyombare ya yi yunkurin hambarar da Pierre Nkurunziza daga gadon mulki. Sai dai rundunar tsaron kasar ta ce wannan yunkurin ya ci tura.Lamarin da ya haddasa wani sabon rikici tsakanin masu goyon bayan tazarcen shugaban kasa da kuma masu adawa da wannan mataki saboda a cewarsu ya sabawa doka.